AhlolBayt News Agency (ABNA)

source : IQNA
Montag

16 März 2020

07:15:05
1017901

China Ta Zargi Amurka Da Yada Cutar Coronta

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar China ya bayyana cewa akwai yiwuwar cewa Amurka ce ta shigo da corona a cikin China.

Wie die Ahlulbayt Nachrichtenagentur ABNA berichtet, Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta China ya bayyana akwai zaton cewa Amurka ce ta shigar da cutar Corona a cikin kasa ta China daga garin Wuhan, inda nan ne cutar ta fara yaduwa, a kan haka China tana bukatar bayani dalla-dalla kan wannan batu daga gwamnatin Amurka.

Ya ce daga cikin bayanin da suke bukata har da neman sanin adadin Amurkawa da suka kamu da cutar da kuma lokacin da suka fara kamuwa, da sunan asibitocin da aka kwantar da su.

Ya kara da cewa zato mafi karfi shi ne cewa, sojojin Amurka ne suka yada wannan cutar a cikin kasar China, a kan haka dole ne Amurak ta fito ta yi gwamnatin China bayani ba tare da wasu kauce-kauce ba.




/129